< Zabura 29 >
1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
Psaume de David. Fils de Dieu, rendez à l’Éternel, Rendez à l’Éternel gloire et honneur!
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
Rendez à l’Éternel gloire pour son nom! Prosternez-vous devant l’Éternel avec des ornements sacrés!
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
La voix de l’Éternel retentit sur les eaux, Le Dieu de gloire fait gronder le tonnerre; L’Éternel est sur les grandes eaux.
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
La voix de l’Éternel est puissante, La voix de l’Éternel est majestueuse.
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
La voix de l’Éternel brise les cèdres; L’Éternel brise les cèdres du Liban,
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
Il les fait bondir comme des veaux, Et le Liban et le Sirion comme de jeunes buffles.
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
La voix de l’Éternel fait jaillir des flammes de feu.
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
La voix de l’Éternel fait trembler le désert; L’Éternel fait trembler le désert de Kadès.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
La voix de l’Éternel fait enfanter les biches, Elle dépouille les forêts. Dans son palais tout s’écrie: Gloire!
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
L’Éternel était sur son trône lors du déluge; L’Éternel sur son trône règne éternellement.
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
L’Éternel donne la force à son peuple; L’Éternel bénit son peuple et le rend heureux.