< Zabura 29 >

1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
Un psaume de David, à l'occasion de l'assemblée solennelle du Tabernacle. Apportez au Seigneur, enfants de Dieu, apportez au Seigneur les petits des béliers.
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
Rendez au Seigneur gloire et honneur; glorifiez le nom du Seigneur; adorez le Seigneur en son saint parvis.
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
La voix du Seigneur est sur les eaux; le Dieu de gloire a tonné; le Seigneur est sur les grandes eaux.
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
La voix du Seigneur est puissante; la voix du Seigneur est pleine de magnificence.
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
La voix du Seigneur brise les cèdres; le Seigneur va broyer les cèdres du Liban.
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
Il les brisera comme un jeune taureau du Liban, comme le faon chéri de la licorne.
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
C'est la voix du Seigneur qui divise la flamme et le feu.
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
C'est la voix du Seigneur qui fait trembler le désert; le Seigneur ébranlera le désert de Cadès.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
C'est la voix du Seigneur qui a préparé la naissance des cerfs; elle découvrira les forêts, et dans le temple du Seigneur chacun dira sa gloire.
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
Le Seigneur répandra sur la terre un déluge; le Seigneur est roi, et il siégera éternellement.
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
Le Seigneur fortifiera son peuple; le Seigneur bénira son peuple en lui donnant la paix.

< Zabura 29 >