< Zabura 29 >

1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
Daavidin virsi. Antakaa Herralle, te Jumalan pojat, antakaa Herralle kunnia ja väkevyys.
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
Antakaa Herralle hänen nimensä kunnia, kumartakaa Herraa pyhässä kaunistuksessa.
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
Herran ääni käy vetten päällä; kunnian Jumala jylisee, Herra suurten vetten päällä.
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
Herran ääni käy voimallisesti, Herran ääni käy valtavasti.
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
Herran ääni särkee setrit, Herra särkee Libanonin setrit.
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
Hän hypittää niitä niinkuin vasikkaa, Libanonia ja Sirjonia niinkuin nuorta villihärkää.
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
Herran ääni halkoo tulen liekit.
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
Herran ääni vapisuttaa erämaan, Herra vapisuttaa Kaadeksen erämaan.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
Herran ääni saattaa peurat poikimaan, se raastaa paljaiksi metsät. Ja kaikki hänen temppelissänsä sanoo: "Kunnia!"
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
Herra istui valtaistuimellaan, ja vedenpaisumus tuli. Herra istuu kuninkaana iankaikkisesti.
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
Herra antaa kansallensa väkevyyden, Herra siunaa kansaansa rauhalla.

< Zabura 29 >