< Zabura 29 >

1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
“A psalm of David.” Give to Jehovah, O ye sons of God! Give to Jehovah glory and praise!
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
Give to Jehovah the glory due to his name; Worship Jehovah in holy attire!
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
The voice of Jehovah is heard above the waters; The God of glory thundereth, -Jehovah above the great waters.
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
The voice of Jehovah is powerful; The voice of Jehovah is full of majesty;
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
The voice of Jehovah breaketh the cedars; Yea, Jehovah breaketh the cedars of Lebanon;
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
Yea, he maketh them to leap like a calf, —Lebanon and Sirion like a young buffalo.
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
The voice of Jehovah divideth the flames of fire.
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
The voice of Jehovah maketh the wilderness tremble; Yea, Jehovah maketh the wilderness of Kadesh tremble.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
The voice of Jehovah maketh the hinds bring forth, And layeth bare the forests; While, in his palace, every one declareth his glory.
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
Jehovah sitteth above the flood; Yea, Jehovah sitteth king for ever.
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
Jehovah will give strength to his people; Jehovah will bless his people with peace.

< Zabura 29 >