< Zabura 29 >
1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
A PSALM OF DAVID. Ascribe to YHWH, you sons of the mighty, Ascribe to YHWH glory and strength.
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
Ascribe to YHWH the glory of His Name, Bow yourselves to YHWH, In the beauty of holiness.
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
The voice of YHWH [is] on the waters, The God of glory has thundered, YHWH [is] on many waters.
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
The voice of YHWH [is] with power, The voice of YHWH [is] with majesty,
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
The voice of YHWH [is] shattering cedars, Indeed, YHWH shatters the cedars of Lebanon.
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
And He causes them to skip as a calf, Lebanon and Sirion as a son of Reems,
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
The voice of YHWH is hewing fiery flames,
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
The voice of YHWH pains a wilderness, YHWH pains the wilderness of Kadesh.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
The voice of YHWH pains the oaks, And makes bare the forests, And in His temple everyone says, “Glory!”
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
YHWH has sat on the flood, And YHWH sits [as] king for all time,
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
YHWH gives strength to His people, YHWH blesses His people with peace!