< Zabura 29 >

1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
A Psalm of David. Ascribe unto the LORD, O ye sons of might, ascribe unto the LORD glory and strength.
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
Ascribe unto the LORD the glory due unto His name; worship the LORD in the beauty of holiness.
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
The voice of the LORD is upon the waters; the God of glory thundereth, even the LORD upon many waters.
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
The voice of the LORD is powerful; the voice of the LORD is full of majesty.
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
The voice of the LORD breaketh the cedars; yea, the LORD breaketh in pieces the cedars of Lebanon.
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
He maketh them also to skip like a calf; Lebanon and Sirion like a young wild-ox.
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
The voice of the LORD heweth out flames of fire.
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
The voice of the LORD shaketh the wilderness; the LORD shaketh the wilderness of Kadesh.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
The voice of the LORD maketh the hinds to calve, and strippeth the forests bare; and in His temple all say: 'Glory.'
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
The LORD sat enthroned at the flood; yea, the LORD sitteth as King for ever.
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
The LORD will give strength unto His people; the LORD will bless his people with peace.

< Zabura 29 >