< Zabura 29 >

1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
A Psalm of David [on the occasion] of the solemn assembly of the Tabernacle. Bring to the Lord, ye sons of God, bring to the Lord young rams; bring to the Lord glory and honour.
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
Bring to the Lord glory, [due] to his name; worship the lord in his holy court.
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
The voice of the Lord is upon the waters: the God of glory has thundered: the Lord is upon many waters.
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
The voice of the Lord is mighty; the voice of the Lord is full of majesty.
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
[There is] the voice of the Lord who breaks the cedars; the Lord will break the cedars of Libanus.
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
And he will beat them small, [even] Libanus itself, like a calf; and the beloved one is as a young unicorn.
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
[There is] a voice of the Lord who divides a flame of fire.
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
A voice of the Lord who shakes the wilderness; the Lord will shake the wilderness of Cades.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
The voice of the Lord strengthens the hinds, and will uncover the thickets: and in his temple every one speaks [of his] glory.
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
The Lord will dwell on the waterflood: and the Lord will sit a king for ever.
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
The Lord will give strength to his people; the Lord will bless his people with peace.

< Zabura 29 >