< Zabura 29 >

1 Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
Žalm Davidův. Vzdejte Hospodinu, velikomocní, vzdejte Hospodinu čest a sílu.
2 Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
Vzdejte Hospodinu slávu jména jeho, sklánějte se Hospodinu v ozdobě svatosti.
3 Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
Hlas Hospodinův nad vodami, Bůh silný slávy hřímání vzbuzuje, Hospodin to činí nad vodami mnohými.
4 Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
Hlas Hospodinův přichází s mocí, hlas Hospodinův s velebností.
5 Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
Hlas Hospodinův láme cedry, rozrážíť Hospodin cedry Libánské.
6 Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
A činí, aby skákali jako telata, Libán a Sirion, jako mladý jednorožec.
7 Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
Hlas Hospodinův rozkřesává plamen ohně.
8 Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
Hlas Hospodinův k bolesti přivodí poušť, k bolesti přivodí Hospodin poušť Kádes.
9 Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
Hlas Hospodinův to činí, že laně plodu pozbývají, obnažuje i lesy, ale v chrámě svém všecku svou slávu vypravuje.
10 Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
Hospodin nad potopou seděl, a budeť seděti Hospodin, jsa králem i na věky.
11 Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.
Hospodin silou lid svůj daří, Hospodin požehná lidu svému v pokoji.

< Zabura 29 >