< Zabura 28 >

1 Ta Dawuda. A gare ka nake kira, ya Ubangiji Dutsena; kada ka yi mini kunnen ƙashi. Gama in ka yi shiru, zan zama kamar waɗanda suka gangara rami.
Ngiyakhala kuwe, Nkosi; dwala lami, ungangithuleli, hlezi nxa ungithulela, ngifanane labehlela emgodini.
2 Ka ji kukata ta neman jinƙai yayinda nake kira ka don neman taimako, yayinda nake daga hannuwana wajen Wurinka Mafi Tsarki.
Zwana ilizwi lokuncenga kwami lapho ngikhala kuwe, lapho ngiphakamisela izandla zami endaweni yakho yelizwi engcwele.
3 Kada ka ja ni tare da mugaye, tare da masu yin mugunta, masu magana kamar ta alheri ce da maƙwabtansu amma suna riƙe da su a zukatansu.
Ungangihuduli kanye lababi njalo kanye labenzi bobubi, abakhuluma ukuthula labomakhelwane babo, kodwa ububi busenhliziyweni yabo.
4 Ka sāka musu da ayyukansu da kuma don mugun aikinsu; ka sāka musu saboda abin da hannuwansu suka yi ka kuma mayar musu abin da ya dace da su.
Ubanike njengokwenza kwabo, lanjengobubi bezenzo zabo; ubanike njengokomsebenzi wezandla zabo, ubabuyisele isenzo sabo.
5 Da yake ba su kula da ayyukan Ubangiji da abin da hannuwansa suka yi ba, zai rushe su ba kuwa zai ƙara gina su ba.
Ngoba kabayinanzi imisebenzi yeNkosi lokwenza kwezandla zayo, izababhidliza ingabakhi.
6 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya ji kukata na neman jinƙai.
Kayibongwe iNkosi, ngoba ilizwile ilizwi lokuncenga kwami.
7 Ubangiji shi ne ƙarfina da garkuwata; zuciyata ta amince da shi, kuma na sami taimako. Zuciyata ta yi tsalle don farin ciki zan kuwa yi godiya gare shi cikin waƙa.
INkosi ingamandla ami lesihlangu sami; inhliziyo yami ithembela kuyo, ngiyasizwa; ngakho inhliziyo yami iyathokoza, ngiyidumise ngengoma yami.
8 Ubangiji shi ne ƙarfin mutanensa, kagarar ceto domin shafaffensa.
INkosi ingamandla abo, njalo iyinqaba yezinsindiso zogcotshiweyo wayo.
9 Ka cece mutanenka ka kuma albarkace gādonka; ka zama mai kiwonsu ka kuma riƙe su har abada.
Sindisa abantu bakho, ubusise ilifa lakho, beluse, ubaphakamise kuze kube nininini.

< Zabura 28 >