< Zabura 28 >

1 Ta Dawuda. A gare ka nake kira, ya Ubangiji Dutsena; kada ka yi mini kunnen ƙashi. Gama in ka yi shiru, zan zama kamar waɗanda suka gangara rami.
De David. Éternel! C’est à toi que je crie. Mon rocher! Ne reste pas sourd à ma voix, De peur que, si tu t’éloignes sans me répondre, Je ne sois semblable à ceux qui descendent dans la fosse.
2 Ka ji kukata ta neman jinƙai yayinda nake kira ka don neman taimako, yayinda nake daga hannuwana wajen Wurinka Mafi Tsarki.
Écoute la voix de mes supplications, quand je crie à toi, Quand j’élève mes mains vers ton sanctuaire.
3 Kada ka ja ni tare da mugaye, tare da masu yin mugunta, masu magana kamar ta alheri ce da maƙwabtansu amma suna riƙe da su a zukatansu.
Ne m’emporte pas avec les méchants et les hommes iniques, Qui parlent de paix à leur prochain et qui ont la malice dans le cœur.
4 Ka sāka musu da ayyukansu da kuma don mugun aikinsu; ka sāka musu saboda abin da hannuwansu suka yi ka kuma mayar musu abin da ya dace da su.
Rends-leur selon leurs œuvres et selon la malice de leurs actions, Rends-leur selon l’ouvrage de leurs mains; Donne-leur le salaire qu’ils méritent.
5 Da yake ba su kula da ayyukan Ubangiji da abin da hannuwansa suka yi ba, zai rushe su ba kuwa zai ƙara gina su ba.
Car ils ne sont pas attentifs aux œuvres de l’Éternel, A l’ouvrage de ses mains. Qu’il les renverse et ne les relève point!
6 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya ji kukata na neman jinƙai.
Béni soit l’Éternel! Car il exauce la voix de mes supplications.
7 Ubangiji shi ne ƙarfina da garkuwata; zuciyata ta amince da shi, kuma na sami taimako. Zuciyata ta yi tsalle don farin ciki zan kuwa yi godiya gare shi cikin waƙa.
L’Éternel est ma force et mon bouclier; En lui mon cœur se confie, et je suis secouru; J’ai de l’allégresse dans le cœur, Et je le loue par mes chants.
8 Ubangiji shi ne ƙarfin mutanensa, kagarar ceto domin shafaffensa.
L’Éternel est la force de son peuple, Il est le rocher des délivrances de son oint.
9 Ka cece mutanenka ka kuma albarkace gādonka; ka zama mai kiwonsu ka kuma riƙe su har abada.
Sauve ton peuple et bénis ton héritage! Sois leur berger et leur soutien pour toujours!

< Zabura 28 >