< Zabura 28 >

1 Ta Dawuda. A gare ka nake kira, ya Ubangiji Dutsena; kada ka yi mini kunnen ƙashi. Gama in ka yi shiru, zan zama kamar waɗanda suka gangara rami.
De David. Éternel! je crie à toi; mon rocher! ne te tais point envers moi; de peur que, si tu gardes le silence envers moi, je ne sois fait semblable à ceux qui descendent dans la fosse.
2 Ka ji kukata ta neman jinƙai yayinda nake kira ka don neman taimako, yayinda nake daga hannuwana wajen Wurinka Mafi Tsarki.
Écoute la voix de mes supplications quand je crie à toi, quand j’élève mes mains vers l’oracle de ta sainteté.
3 Kada ka ja ni tare da mugaye, tare da masu yin mugunta, masu magana kamar ta alheri ce da maƙwabtansu amma suna riƙe da su a zukatansu.
Ne m’entraîne pas avec les méchants, ni avec les ouvriers d’iniquité, qui parlent paix avec leur prochain, tandis que la méchanceté est dans leur cœur.
4 Ka sāka musu da ayyukansu da kuma don mugun aikinsu; ka sāka musu saboda abin da hannuwansu suka yi ka kuma mayar musu abin da ya dace da su.
Donne-leur selon leur œuvre et selon l’iniquité de leurs actions; donne-leur selon l’ouvrage de leurs mains, rends-leur selon ce qu’ils ont fait.
5 Da yake ba su kula da ayyukan Ubangiji da abin da hannuwansa suka yi ba, zai rushe su ba kuwa zai ƙara gina su ba.
Parce qu’ils ne discernent pas les œuvres de l’Éternel, ni l’ouvrage de ses mains, il les détruira et ne les édifiera point.
6 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya ji kukata na neman jinƙai.
Béni soit l’Éternel! car il a entendu la voix de mes supplications.
7 Ubangiji shi ne ƙarfina da garkuwata; zuciyata ta amince da shi, kuma na sami taimako. Zuciyata ta yi tsalle don farin ciki zan kuwa yi godiya gare shi cikin waƙa.
L’Éternel est ma force et mon bouclier; en lui mon cœur a eu sa confiance, et j’ai été secouru; et mon cœur se réjouit, et je le célébrerai dans mon cantique.
8 Ubangiji shi ne ƙarfin mutanensa, kagarar ceto domin shafaffensa.
L’Éternel est leur force, et il est le lieu fort des délivrances de son oint.
9 Ka cece mutanenka ka kuma albarkace gādonka; ka zama mai kiwonsu ka kuma riƙe su har abada.
Sauve ton peuple, et bénis ton héritage; et pais-les, et élève-les pour toujours.

< Zabura 28 >