< Zabura 28 >

1 Ta Dawuda. A gare ka nake kira, ya Ubangiji Dutsena; kada ka yi mini kunnen ƙashi. Gama in ka yi shiru, zan zama kamar waɗanda suka gangara rami.
[A Psalm] of David. To thee will I cry, O LORD my rock; be not silent to me: lest, [if] thou shouldst be silent to me, I should become like them that go down into the pit.
2 Ka ji kukata ta neman jinƙai yayinda nake kira ka don neman taimako, yayinda nake daga hannuwana wajen Wurinka Mafi Tsarki.
Hear the voice of my supplications, when I cry to thee, when I lift my hands towards thy holy oracle.
3 Kada ka ja ni tare da mugaye, tare da masu yin mugunta, masu magana kamar ta alheri ce da maƙwabtansu amma suna riƙe da su a zukatansu.
Draw me not away with the wicked, and with the workers of iniquity, who speak peace to their neighbors, but mischief [is] in their hearts.
4 Ka sāka musu da ayyukansu da kuma don mugun aikinsu; ka sāka musu saboda abin da hannuwansu suka yi ka kuma mayar musu abin da ya dace da su.
Give them according to their deeds, and according to the wickedness of their endeavors: give them after the work of their hands; render to them their desert.
5 Da yake ba su kula da ayyukan Ubangiji da abin da hannuwansa suka yi ba, zai rushe su ba kuwa zai ƙara gina su ba.
Because they regard not the works of the LORD, nor the operation of his hands, he will destroy them, and not build them up.
6 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya ji kukata na neman jinƙai.
Blessed [be] the LORD, because he hath heard the voice of my supplications.
7 Ubangiji shi ne ƙarfina da garkuwata; zuciyata ta amince da shi, kuma na sami taimako. Zuciyata ta yi tsalle don farin ciki zan kuwa yi godiya gare shi cikin waƙa.
The LORD [is] my strength, and my shield; my heart trusted in him, and I am helped: therefore my heart greatly rejoiceth; and with my song will I praise him.
8 Ubangiji shi ne ƙarfin mutanensa, kagarar ceto domin shafaffensa.
The LORD [is] their strength, and he [is] the saving strength of his anointed.
9 Ka cece mutanenka ka kuma albarkace gādonka; ka zama mai kiwonsu ka kuma riƙe su har abada.
Save thy people, and bless thy inheritance: feed them also, and lift them up for ever.

< Zabura 28 >