< Zabura 28 >
1 Ta Dawuda. A gare ka nake kira, ya Ubangiji Dutsena; kada ka yi mini kunnen ƙashi. Gama in ka yi shiru, zan zama kamar waɗanda suka gangara rami.
BY DAVID. To You, O YHWH, I call, My rock, do not be silent to me! Lest You are silent to me, And I have been compared With those going down to the pit.
2 Ka ji kukata ta neman jinƙai yayinda nake kira ka don neman taimako, yayinda nake daga hannuwana wajen Wurinka Mafi Tsarki.
Hear the voice of my supplications, In my crying to You, In my lifting up my hands toward your holy oracle.
3 Kada ka ja ni tare da mugaye, tare da masu yin mugunta, masu magana kamar ta alheri ce da maƙwabtansu amma suna riƙe da su a zukatansu.
Do not draw me with the wicked, And with workers of iniquity, Speaking peace with their neighbors, And evil in their heart.
4 Ka sāka musu da ayyukansu da kuma don mugun aikinsu; ka sāka musu saboda abin da hannuwansu suka yi ka kuma mayar musu abin da ya dace da su.
Give to them according to their acting, And according to the evil of their doings. Give to them according to the work of their hands. Return their deed to them.
5 Da yake ba su kula da ayyukan Ubangiji da abin da hannuwansa suka yi ba, zai rushe su ba kuwa zai ƙara gina su ba.
For they do not attend to the doing of YHWH, And to the work of His hands. He throws them down, And does not build them up.
6 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya ji kukata na neman jinƙai.
Blessed [is] YHWH, For He has heard the voice of my supplications.
7 Ubangiji shi ne ƙarfina da garkuwata; zuciyata ta amince da shi, kuma na sami taimako. Zuciyata ta yi tsalle don farin ciki zan kuwa yi godiya gare shi cikin waƙa.
YHWH [is] my strength, and my shield, In Him my heart trusted, and I have been helped. And my heart exults, And I thank Him with my song.
8 Ubangiji shi ne ƙarfin mutanensa, kagarar ceto domin shafaffensa.
YHWH [is] strength to him, Indeed, the strength of the salvation of His anointed [is] He.
9 Ka cece mutanenka ka kuma albarkace gādonka; ka zama mai kiwonsu ka kuma riƙe su har abada.
Save Your people, and bless Your inheritance, And feed them, and carry them for all time!