< Zabura 28 >
1 Ta Dawuda. A gare ka nake kira, ya Ubangiji Dutsena; kada ka yi mini kunnen ƙashi. Gama in ka yi shiru, zan zama kamar waɗanda suka gangara rami.
Af David. Herre! til dig vil jeg raabe; min Klippe! vær ikke tavs imod mig, at du ikke holder dig stille imod mig, og jeg bliver lig dem, som fare ned i Graven.
2 Ka ji kukata ta neman jinƙai yayinda nake kira ka don neman taimako, yayinda nake daga hannuwana wajen Wurinka Mafi Tsarki.
Hør mine ydmyge Begæringers Røst, naar jeg raaber til dig, naar jeg opløfter mine Hænder til dit hellige Kor.
3 Kada ka ja ni tare da mugaye, tare da masu yin mugunta, masu magana kamar ta alheri ce da maƙwabtansu amma suna riƙe da su a zukatansu.
Bortriv mig ikke med de ugudelige og med dem, som gøre Uret, dem, som tale Fred med deres Næste, enddog der er ondt i deres Hjerte.
4 Ka sāka musu da ayyukansu da kuma don mugun aikinsu; ka sāka musu saboda abin da hannuwansu suka yi ka kuma mayar musu abin da ya dace da su.
Giv dem efter deres Gerning og efter deres Idrætters Ondskab; giv dem efter deres Hænders Gerning, betal dem, hvad de have fortjent.
5 Da yake ba su kula da ayyukan Ubangiji da abin da hannuwansa suka yi ba, zai rushe su ba kuwa zai ƙara gina su ba.
Thi de agte ikke paa Herrens Værk, ej heller paa hans Hænders Gerning; han skal nedbryde dem og ikke bygge dem op.
6 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya ji kukata na neman jinƙai.
Lovet være Herren; thi han har hørt mine ydmyge Begæringers Røst.
7 Ubangiji shi ne ƙarfina da garkuwata; zuciyata ta amince da shi, kuma na sami taimako. Zuciyata ta yi tsalle don farin ciki zan kuwa yi godiya gare shi cikin waƙa.
Herren er min Styrke og mit Skjold, mit Hjerte har forladt sig paa ham, og jeg er bleven hjulpen; og mit Hjerte fryder sig, og jeg vil takke ham med min Sang.
8 Ubangiji shi ne ƙarfin mutanensa, kagarar ceto domin shafaffensa.
Herren er deres Styrke, og han er sin Salvedes Værn til Frelse.
9 Ka cece mutanenka ka kuma albarkace gādonka; ka zama mai kiwonsu ka kuma riƙe su har abada.
Frels dit Folk og velsign din Arv og fød dem og ophøj dem indtil evig Tid.