< Zabura 27 >
1 Ta Dawuda. Ubangiji ne haskena da cetona, wa zan ji tsoro? Ubangiji ne mafakar raina, wane ne zan ji tsoro?
Por David. Yahweh é minha luz e minha salvação. A quem devo temer? Yahweh é a força da minha vida. De quem devo ter medo?
2 Sa’ad da mugaye suka tasar mini don su cinye ni, sa’ad da abokan gābana da maƙiyina suka kawo mini hari, sun yi tuntuɓe suka fāɗi.
Quando os malfeitores vieram até mim para comer minha carne, mesmo meus adversários e meus inimigos, eles tropeçaram e caíram.
3 Ko da yake mayaƙa sun kewaye ni, zuciyata ba za tă ji tsoro ba; ko da yake ya ɓarke a kaina, duk da haka zan ƙarfafa.
Embora um exército deva acampar contra mim, meu coração não deve temer. Embora a guerra deva se levantar contra mim, mesmo assim, estarei confiante.
4 Abu guda na roƙi Ubangiji, wannan shi ne na nema, cewa in zauna a gidan Ubangiji dukan kwanakin raina, in dubi kyan Ubangiji in kuma neme shi a cikin haikalinsa.
Uma coisa que pedi a Yahweh, que vou procurar: que eu possa morar na casa de Yahweh todos os dias da minha vida, para ver a beleza de Yahweh, e para inquirir em seu templo.
5 Gama a lokacin wahala, zai kiyaye ni lafiya a wurin zamansa; zai ɓoye ni cikin inuwar tabanakul nasa ya kuma sa ni can a bisa dutse.
Pois no dia dos problemas, ele me manterá em segredo em seu pavilhão. No lugar secreto de seu tabernáculo, ele vai me esconder. Ele me levantará sobre uma rocha.
6 Sa’an nan kaina zai ɗaukaka a bisa abokan gābana waɗanda suka kewaye ni; a tabanakul nasa zan miƙa hadaya da sowa ta farin ciki; zan rera in kuma yi kiɗi ga Ubangiji.
Agora minha cabeça será erguida acima de meus inimigos ao meu redor. Oferecerei sacrifícios de alegria em sua tenda. Cantarei, sim, cantarei louvores a Yahweh.
7 Ka ji muryata sa’ad da na yi kira, ya Ubangiji; ka yi mini jinƙai ka kuma amsa mini.
Ouça, Yahweh, quando choro com minha voz. Tenha piedade também de mim, e me responda.
8 Zuciyata kan faɗa game da kai, “Nemi fuskarsa!” Fuskarka, Ubangiji, zan nema.
Quando você disse: “Procure meu rosto”... meu coração lhe disse: “Vou procurar seu rosto, Yahweh”.
9 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni, kada ka kore bawanka daga gare ka cikin fushi; kai ne ka kasance mai taimakona. Kada ka ƙi ni ko ka yashe ni, Ya Allah Mai cetona.
Não esconda seu rosto de mim. Não guarde seu criado com raiva. Você tem sido minha ajuda. Não me abandone, nem me abandona, Deus da minha salvação.
10 Ko da mahaifina da mahaifiyata sun yashe ni, Ubangiji zai karɓe ni.
Quando meu pai e minha mãe me abandonam, então Yahweh me aceitará.
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji; ka bi da ni a miƙaƙƙiyar hanya saboda masu danne ni.
Ensina-me à tua maneira, Yahweh. Conduza-me em um caminho reto, por causa de meus inimigos.
12 Kada ka ba da ni da sha’awar maƙiyina, gama masu shaidar ƙarya sun taso a kaina, suna numfasa tashin hankali.
Não me entregue ao desejo dos meus adversários, por falsas testemunhas se terem levantado contra mim, como, por exemplo, expirar a crueldade.
13 Har yanzu ina da ƙarfin gwiwa a wannan cewa zan ga alherin Ubangiji; a ƙasar masu rai.
Ainda tenho confiança nisso: Verei a bondade de Yahweh na terra dos vivos.
14 Ka dogara ga Ubangiji, ka yi ƙarfin hali ka yi ƙarfin zuciya ka kuma dogara ga Ubangiji.
Espere por Yahweh. Seja forte, e deixe seu coração tomar coragem. Sim, espere por Yahweh.