< Zabura 27 >

1 Ta Dawuda. Ubangiji ne haskena da cetona, wa zan ji tsoro? Ubangiji ne mafakar raina, wane ne zan ji tsoro?
A psalm of David. The Lord is my light and my saviour; whom then should I fear? The Lord protects my life; whom then should I dread?
2 Sa’ad da mugaye suka tasar mini don su cinye ni, sa’ad da abokan gābana da maƙiyina suka kawo mini hari, sun yi tuntuɓe suka fāɗi.
When the wicked drew near to assail me and eat up my flesh, it was those who distressed and opposed me who stumbled and fell.
3 Ko da yake mayaƙa sun kewaye ni, zuciyata ba za tă ji tsoro ba; ko da yake ya ɓarke a kaina, duk da haka zan ƙarfafa.
Though against me a host should encamp, yet my heart would be fearless: though battle should rise up against me, still would I be trustful.
4 Abu guda na roƙi Ubangiji, wannan shi ne na nema, cewa in zauna a gidan Ubangiji dukan kwanakin raina, in dubi kyan Ubangiji in kuma neme shi a cikin haikalinsa.
One thing have I asked of the Lord, and that do I long for – To live in the house of the Lord all the days of my life, to gaze on the grace of the Lord and inquire in his temple.
5 Gama a lokacin wahala, zai kiyaye ni lafiya a wurin zamansa; zai ɓoye ni cikin inuwar tabanakul nasa ya kuma sa ni can a bisa dutse.
For he will hide me in his shelter in the day of misfortune. In his sheltering tent he hides me: he lifts me up on a rock.
6 Sa’an nan kaina zai ɗaukaka a bisa abokan gābana waɗanda suka kewaye ni; a tabanakul nasa zan miƙa hadaya da sowa ta farin ciki; zan rera in kuma yi kiɗi ga Ubangiji.
And now that my head he has lifted above my encircling foes, I will march round the altar and sacrifice, shouting with joy, in his tent, making music and song to the Lord.
7 Ka ji muryata sa’ad da na yi kira, ya Ubangiji; ka yi mini jinƙai ka kuma amsa mini.
Hear, O Lord, my loud cry, and graciously answer me.
8 Zuciyata kan faɗa game da kai, “Nemi fuskarsa!” Fuskarka, Ubangiji, zan nema.
My heart has said to you, ‘Your face, O Lord, I seek.’
9 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni, kada ka kore bawanka daga gare ka cikin fushi; kai ne ka kasance mai taimakona. Kada ka ƙi ni ko ka yashe ni, Ya Allah Mai cetona.
Hide not your face from me, reject not your servant in anger: for you have been my help. Abandon me not, nor forsake me, O God of my help:
10 Ko da mahaifina da mahaifiyata sun yashe ni, Ubangiji zai karɓe ni.
for father and mother have left me; but the Lord will take me up.
11 Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji; ka bi da ni a miƙaƙƙiyar hanya saboda masu danne ni.
Teach me your way, O Lord: lead me in an even path, because of my enemies.
12 Kada ka ba da ni da sha’awar maƙiyina, gama masu shaidar ƙarya sun taso a kaina, suna numfasa tashin hankali.
Give me not up, O Lord, unto the rage of my foes; for against me have risen false witnesses, breathing out cruelty.
13 Har yanzu ina da ƙarfin gwiwa a wannan cewa zan ga alherin Ubangiji; a ƙasar masu rai.
Firm is the faith I cherish, that I, in the land of the living, will yet see the goodness of God.
14 Ka dogara ga Ubangiji, ka yi ƙarfin hali ka yi ƙarfin zuciya ka kuma dogara ga Ubangiji.
Let your heart be courageous and strong, and wait on the Lord.

< Zabura 27 >