< Zabura 25 >
1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
Davut'un mezmuru Ya RAB, bütün varlığımla sana yaklaşıyorum,
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
Ey Tanrım, sana güveniyorum, utandırma beni, Düşmanlarım zafer kahkahası atmasın!
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Sana umut bağlayan hiç kimse utanca düşmez; Nedensiz hainlik edenler utanır.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Ya RAB, yollarını bana öğret, Yönlerini bildir.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Bana gerçek yolunda öncülük et, eğit beni; Çünkü beni kurtaran Tanrı sensin. Bütün gün umudum sende.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Ya RAB, sevecenliğini ve sevgini anımsa; Çünkü onlar öncesizlikten beri aynıdır.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Gençlik günahlarımı, isyanlarımı anımsama, Sevgine göre anımsa beni, Çünkü sen iyisin, ya RAB.
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
RAB iyi ve doğrudur, Onun için günahkârlara yol gösterir.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
Alçakgönüllülere adalet yolunda öncülük eder, Kendi yolunu öğretir onlara.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
RAB'bin bütün yolları sevgi ve sadakate dayanır Antlaşmasındaki buyruklara uyanlar için.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
Ya RAB, adın uğruna Suçumu bağışla, çünkü suçum büyük.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
Kim RAB'den korkarsa, RAB ona seçeceği yolu gösterir.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
Gönenç içinde yaşayacak o insan, Soyu ülkeyi sahiplenecek.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
RAB kendisinden korkanlarla paylaşır sırrını, Onlara açıklar antlaşmasını.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Gözlerim hep RAB'dedir, Çünkü ayaklarımı ağdan O çıkarır.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Halime bak, lütfet bana; Çünkü garip ve mazlumum.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
Yüreğimdeki sıkıntılar artıyor, Kurtar beni dertlerimden!
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Üzüntüme, acılarıma bak, Bütün günahlarımı bağışla!
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Düşmanlarıma bak, ne kadar çoğaldılar, Nasıl da benden nefret ediyorlar!
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Canımı koru, kurtar beni! Hayal kırıklığına uğratma, çünkü sana sığınıyorum!
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Dürüstlük, doğruluk korusun beni, Çünkü umudum sendedir.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Ey Tanrı, kurtar İsrail'i Bütün sıkıntılarından!