< Zabura 25 >

1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
Kwako, Yahwe, nayainua maisha yangu!
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
Mungu wangu, ninaamini katika wewe. Usiniache niaibishwe; usiwaache maadui zangu wafurahie ushindi wao kwangu.
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Asiaibishwe mtu yeyote anaye kutumaini bali waaibishwe wale watendao hila bila sababu!
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Unijulishe njia zako, Yahwe; unifundishe njia zako.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Uniongoze kwenye kweli yako na unifundishe, kwa kuwa wewe ni Mungu wa wokovu wangu; ninakutumainia wewe siku zote za maisha yangu.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Kumbuka, Yahwe, matendo yako ya huruma na uaminifu wa agano lako; kwa kuwa vimekuwapo siku zote.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Usizikumbuke dhambi za ujana wangu wala uasi wangu; Uniweke akilini mwako pamoja na uaminifu wa agano kwa zababu ya uzuri wa wako, Yahwe!
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Yahwe ni mzuri na mwenye haki; kwa hiyo yeye huwafundisha njia mwenye dhambi.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
Yeye huwaelekeza wanyenyekevu kwa kile kilicho sahihi na yeye huwafundisha wao njia yake.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
Njia zote za Yahwe ni za upendo wa kudumu na niaminifu kwa wote wanao tunza agano na maagizo ya amri zake.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
Kwa ajili ya jina lako, Yahwe, unisamehe dhambi zangu, kwa kuwa ni nyingi mno.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
Ni nani ambaye anamuogopa Yahwe? Bwana atamfundisha yeye katika njia ambayo anapaswa kuichagua.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
Maisha yake yataenenda katika uzuri; na uzao wake utairithi nchi.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
Urafiki wa Yahwe ni kwa ajili ya wale wanao mheshimu yeye, naye hulifanya agano lake lijulikane kwao.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Siku zote macho yangu yanamtazama Yahwe, kwa kuwa yeye ataifungua miguu yangu kwenye nyavu.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Unigeukie mimi na unihurumie; kwa maana niko peke yangu na niliye matesoni.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
Maumivu ya moyo wangu yameongezeka; uniondoe katika dhiki hii!
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Tazama mateso yangu na taabu yangu; unisamehe dhambi zangu zote.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Ona maadui zangu, kwa maana ni wengi; wananichukia kwa chuki ya kikatili.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Uyalinde maisha yangu na uniokoe; usiniache niaibishwe, Kwa kuwa kwako nakimbilia usalama!
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Uadilifu na unyofu vinihifadhi, kwa kuwa nina kutumainia wewe.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Mungu, uiokoe Israeli, na shida yake yote!

< Zabura 25 >