< Zabura 25 >

1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
Salmo de David. A TI, oh Jehová, levantaré mi alma.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
Dios mío, en ti confío; no sea yo avergonzado, no se alegren de mí mis enemigos.
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Ciertamente ninguno de cuantos en ti esperan será confundido: serán avergonzados los que se rebelan sin causa.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Muéstrame, oh Jehová, tus caminos; enséñame tus sendas.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Encamíname en tu verdad, y enséñame; porque tú eres el Dios de mi salud: en ti he esperado todo el día.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Acuérdate, oh Jehová, de tus conmiseraciones y de tus misericordias, que son perpetuas.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
De los pecados de mi mocedad, y de mis rebeliones, no te acuerdes; conforme á tu misericordia acuérdate de mí, por tu bondad, oh Jehová.
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Bueno y recto es Jehová: por tanto él enseñará á los pecadores el camino.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
Encaminará á los humildes por el juicio, y enseñará á los mansos su carrera.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
Todas las sendas de Jehová son misericordia y verdad, para los que guardan su pacto y sus testimonios.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
Por amor de tu nombre, oh Jehová, perdonarás también mi pecado; porque es grande.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
¿Quién es el hombre que teme á Jehová? El le enseñará el camino que ha de escoger.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
Su alma reposará en el bien, y su simiente heredará la tierra.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
El secreto de Jehová es para los que le temen; y á ellos hará conocer su alianza.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Mis ojos están siempre hacia Jehová; porque él sacará mis pies de la red.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Mírame, y ten misericordia de mí; porque estoy solo y afligido.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
Las angustias de mi corazón se han aumentado: sácame de mis congojas.
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Mira mi aflicción y mi trabajo: y perdona todos mis pecados.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Mira mis enemigos, que se han multiplicado, y con odio violento me aborrecen.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Guarda mi alma, y líbrame: no sea yo avergonzado, porque en ti confié.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Integridad y rectitud me guarden; porque en ti he esperado.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Redime, oh Dios, á Israel de todas sus angustias.

< Zabura 25 >