< Zabura 25 >
1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
A Ti, oh Yavé, levanto mi alma.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
¡ʼElohim mío, en Ti confío! No sea yo avergonzado, No se alegren de mí mis enemigos.
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Ciertamente ninguno de los que confían en Ti será avergonzado. Serán avergonzados los que se rebelan sin causa.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Muéstrame, oh Yavé, tus caminos, Enséñame tus sendas.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Encamíname en tu verdad y enséñame, Porque Tú eres el ʼElohim de mi salvación. En Ti espero todo el día.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Acuérdate, oh Yavé, de tu compasión y de tu misericordia que son perpetuas.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
No te acuerdes de los pecados de mi juventud y de mis transgresiones. Conforme a tu misericordia acuérdate de mí, Por tu bondad, oh Yavé.
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Bueno y justo es Yavé. Él muestra el camino a los pecadores.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
Encamina a los humildes en justicia, Y enseña a los mansos su senda.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
Todas las sendas de Yavé son misericordia y verdad Para los que observan su Pacto y sus Preceptos.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
Por amor a tu Nombre, oh Yavé, Perdonas también mi iniquidad, que es grande.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
¿Quién es el hombre que teme a Yavé? Él le enseñará el camino que debe escoger.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
Su alma gozará de bienestar, Y su descendencia heredará la tierra.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
El secreto de Yavé es para los que le temen. A ellos hará conocer su Pacto.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Mis ojos están siempre fijos en Yavé, Porque Él sacará mis pies de la red.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Mírame y ten misericordia de mí, Porque estoy solo y afligido.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
Las angustias de mi corazón se aumentaron. ¡Sácame de mis congojas!
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Mira mi aflicción y mis fatigas, Y perdona todos mis pecados.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
¡Mira cómo se multiplicaron mis enemigos, Y con violento odio me aborrecen!
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
¡Guarda mi alma y líbrame! No sea yo avergonzado, Porque en Ti me refugio.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Integridad y rectitud me guarden, Porque en Ti espero.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
¡Oh ʼElohim, redime a Israel de todas sus angustias!