< Zabura 25 >

1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
Un Salmo de David. Señor, vengo a adorarte.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
Confío en ti, Dios mío. No dejes que sea humillado, y no dejes que mis enemigos triunfen sobre mí.
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Nadie que confía en ti, será humillado, pero la humillación viene de aquellos que son deshonestos deliberadamente.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Muéstrame tus caminos, Señor; enséñame a seguir tus pasos.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Guíame en tu verdad y enséñame, Porque tú eres el Dios de mi salvación. Todo el día pongo mi confianza en ti.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Recuerda, Señor, que tu compasión y tu amor inefable son eternos.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Por favor, no recuerdes los pecados de mi juventud cuando me rebelé contra ti. En vez de eso, recuérdame conforme tu amor inquebrantable, recuérdame con bondad, Señor.
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
El Señor es bueno y recto. Por eso muestra el camino a los que están perdidos.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
Él guía a los humildes para hacer lo que es correcto, enseñándoles su camino.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
Los caminos del Señor son de verdad y amor para los que cumplen sus acuerdo y siguen sus mandamientos.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
Señor, por quien tú eres, perdona la multitud de mis pecados.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
¿Quiénes son los que respetan al Señor? Él les mostrará el camino a elegir.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
Ellos continuarán siendo prósperos, y sus descendientes heredarán la tierra.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
El Señor es amigo de quienes lo respetan, y les explica su acuerdo.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Siempre miro al Señor, porque Él me rescató cuando estaba atrapado.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Mírame y sé bueno conmigo, porque estoy solo y sufriendo.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
Mis problemas se vuelven cada vez más grandes. Por favor sálvame de esto que estoy viviendo.
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Mira todas mis pruebas y mis problemas. Por favor perdona mis pecados.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
¡Mira cuántos enemigos tengo, y cuánto me odian!
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
¡Por favor, mírame y sálvame! No dejes que sea humillado, porque eres el único que me protege.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Que la integridad y la honestidad me defiendan, porque puse mi confianza en ti.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
¡Dios, por favor libera a todo el pueblo de Israel de sus problemas!

< Zabura 25 >