< Zabura 25 >

1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
K tebi, oh Gospod, vzdigujem svojo dušo.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
Oh moj Bog, jaz zaupam vate. Naj ne bom osramočen, naj moji sovražniki ne slavijo zmage nad menoj.
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Da, naj ne bo osramočen nihče, ki čaka nate. Naj bodo osramočeni, ki se pregrešijo brez razloga.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Pokaži mi svoje poti, oh Gospod, úči me svojih stezá.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Vodi me v svoji resnici in me úči, kajti ti si Bog rešitve moje duše, nate čakam ves dan.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Spomni se, oh Gospod, svojih nežnih usmiljenj in svojih ljubečih skrbnosti, kajti bile so vedno, od davnine.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Ne spominjaj se grehov moje mladosti niti mojih prestopkov. Glede na svoje usmiljenje se me spominjaj zaradi svoje dobrote, oh Gospod.
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Dober in pošten je Gospod, zato bo grešnike učil na poti.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
Krotke bo usmerjal na sodbo in krotke bo učil svojo pot.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
Vse Gospodove steze so usmiljenje in resnica do teh, ki se držijo njegove zaveze in njegovih pričevanj.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
Zaradi svojega imena, oh Gospod, odpusti mojo krivičnost, kajti ta je velika.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
Kakšen človek je ta, ki se boji Gospoda? Njega bo on učil na poti, ki jo bo on izbral.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
Njegova duša bo prebivala sproščeno in njegovo seme bo podedovalo zemljo.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
Gospodova skrivnost je s tistimi, ki se ga bojijo in pokazal jim bo svojo zavezo.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Moje oči so vedno v smeri Gospoda, kajti moja stopala bo on potegnil iz mreže.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Obrni se k meni in se me usmili, kajti zapuščen sem in prizadet.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
Težave mojega srca so se povečale. O, osvobodi me iz moje stiske.
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Poglej na mojo žalost in mojo bolečino in odpusti vse moje grehe.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Preudari moje sovražnike, kajti mnogo jih je in sovražijo me s krutim sovraštvom.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Oh varuj mojo dušo in me osvobodi. Naj ne bom osramočen, kajti svoje zaupanje polagam vate.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Naj me ohranjata neokrnjenost in poštenost, kajti jaz čakam nate.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Odkupi Izraela, oh Bog, iz vseh njegovih težav.

< Zabura 25 >