< Zabura 25 >

1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
Псалом Давида. К Тебе, Господи, возношу душу мою.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
Боже мой! на Тебя уповаю, да не постыжусь, да не восторжествуют надо мною враги мои,
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
да не постыдятся и все надеющиеся на Тебя: да постыдятся беззаконнующие втуне.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Укажи мне, Господи, пути Твои и научи меня стезям Твоим.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Направь меня на истину Твою и научи меня, ибо Ты Бог спасения моего; на Тебя надеюсь всякий день.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Вспомни щедроты Твои, Господи, и милости Твои, ибо они от века.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Грехов юности моей и преступлений моих не вспоминай; по милости Твоей вспомни меня Ты, ради благости Твоей, Господи!
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Благ и праведен Господь, посему наставляет грешников на путь,
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
направляет кротких к правде, и научает кротких путям Своим.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
Все пути Господни - милость и истина к хранящим завет Его и откровения Его.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
Ради имени Твоего, Господи, прости согрешение мое, ибо велико оно.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
Кто есть человек, боящийся Господа? Ему укажет Он путь, который избрать.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
Душа его пребудет во благе, и семя его наследует землю.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
Тайна Господня - боящимся Его, и завет Свой Он открывает им.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Очи мои всегда к Господу, ибо Он извлекает из сети ноги мои.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Призри на меня и помилуй меня, ибо я одинок и угнетен.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
Скорби сердца моего умножились; выведи меня из бед моих,
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
призри на страдание мое и на изнеможение мое и прости все грехи мои.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Посмотри на врагов моих, как много их, и какою лютою ненавистью они ненавидят меня.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Сохрани душу мою и избавь меня, да не постыжусь, что я на Тебя уповаю.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Непорочность и правота да охраняют меня, ибо я на Тебя надеюсь.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Избавь, Боже, Израиля от всех скорбей его.

< Zabura 25 >