< Zabura 25 >

1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
A ti, Senhor, levanto a minha alma.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
Deus meu, em ti confio, não me deixes confundido, nem que os meus inimigos triunfem sobre mim.
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Como, na verdade, não serão confundidos os que esperam em ti; confundidos serão os que transgridem sem causa.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Faz-me saber os teus caminhos, Senhor; ensina-me as tuas veredas.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Guia-me na tua verdade, e ensina-me, pois tu és o Deus da minha salvação; por ti estou esperando todo o dia.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Lembra-te, Senhor, das tuas misericórdias e das tuas benignidades, porque são desde a eternidade.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Não te lembres dos pecados da minha mocidade, nem das minhas transgressões: mas segundo a tua misericórdia, lembra-te de mim, por tua bondade, Senhor.
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Bom e reto é o Senhor: pelo que ensinará o caminho aos pecadores.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
Guiará os mansos em direitura: e aos mansos ensinará o seu caminho.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
Todas as veredas do Senhor são misericórdia e verdade para aqueles que guardam o seu concerto e os seus testemunhos.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
Por amor do teu nome, Senhor, perdoa a minha iniquidade, pois é grande.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
Qual é o homem que teme ao Senhor? ele o ensinará no caminho que deve escolher.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
A sua alma pousará no bem, e a sua semente herdará a terra.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
O segredo do Senhor é com aqueles que o temem; e ele lhes mostrará o seu concerto.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Os meus olhos estão continuamente no Senhor, pois ele tirará os meus pés da rede.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Olha para mim, e tem piedade de mim, porque estou solitário e aflito.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
As ancias do meu coração se tem multiplicado: tira-me dos meus apertos.
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Olha para a minha aflição e para a minha dor, e perdoa todos os meus pecados.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Olha para os meus inimigos, pois se vão multiplicando e me aborrecem com ódio cruel.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Guarda a minha alma, e livra-me; não me deixes confundido, porquanto confio em ti.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Guardem-me a sinceridade e a direitura, porquanto espero em ti.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Redime, ó Deus, a Israel de todas as suas angústias.

< Zabura 25 >