< Zabura 25 >

1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
Av David. Til dig, Herre, løfter jeg min sjel.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
Min Gud, til dig har jeg satt min lit; la mig ikke bli til skamme, la ikke mine fiender fryde sig over mig!
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Ja, ingen av dem som bier på dig, skal bli til skamme; de skal bli til skamme som er troløse uten årsak.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Herre, la mig kjenne dine veier, lær mig dine stier!
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Led mig frem i din trofasthet og lær mig! for du er min frelses Gud, på dig bier jeg hele dagen.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Herre, kom din barmhjertighet i hu og din miskunnhets gjerninger! for de er fra evighet.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Kom ikke min ungdoms synder og mine misgjerninger i hu! Kom mig i hu efter din miskunnhet for din godhets skyld, Herre!
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Herren er god og rettvis; derfor lærer han syndere veien.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
Han leder de saktmodige i det som rett er, og lærer de saktmodige sin vei.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
Alle Herrens stier er miskunnhet og trofasthet imot dem som holder hans pakt og hans vidnesbyrd.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
For ditt navns skyld, Herre, forlat mig min misgjerning! for den er stor.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
Hvem er den mann som frykter Herren? Ham lærer han den vei han skal velge.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
Hans sjel skal stadig ha det godt, og hans avkom skal arve landet.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
Herren har fortrolig samfund med dem som frykter ham, og hans pakt skal bli dem kunngjort.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Mine øine er alltid vendt til Herren, for han drar mine føtter ut av garnet.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Vend dig til mig og vær mig nådig! for jeg er enslig og elendig.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
Mitt hjertes angst har de gjort stor; før mig ut av mine trengsler!
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Se min elendighet og min nød, og forlat mig alle mine synder!
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Se mine fiender, de er mange, og de hater mig med urettferdig hat.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Bevar min sjel og redd mig, la mig ikke bli til skamme! for jeg tar min tilflukt til dig.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
La uskyld og opriktighet verge mig! for jeg bier på dig.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Forløs, Gud, Israel av alle dets trengsler!

< Zabura 25 >