< Zabura 25 >
1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
psalmus David ad te Domine levavi animam meam
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
Deus meus in te confido non erubescam
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
neque inrideant me inimici mei etenim universi qui sustinent te non confundentur
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
confundantur omnes iniqua agentes supervacue vias tuas Domine demonstra mihi et semitas tuas doce me
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
dirige me in veritatem tuam et doce me quoniam tu es Deus salvator meus et te sustinui tota die
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
reminiscere miserationum tuarum Domine et misericordiarum tuarum quia a saeculo sunt
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
delicta iuventutis meae et ignorantias meas ne memineris secundum misericordiam tuam memento mei tu; propter bonitatem tuam Domine
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
dulcis et rectus Dominus propter hoc legem dabit delinquentibus in via
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
diriget mansuetos in iudicio docebit mites vias suas
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
universae viae Domini misericordia et veritas requirentibus testamentum eius et testimonia eius
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
propter nomen tuum Domine et propitiaberis peccato meo multum est enim
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
quis est homo qui timet Dominum legem statuet ei in via quam elegit
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
anima eius in bonis demorabitur et semen ipsius hereditabit terram
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
firmamentum est Dominus timentibus eum et testamentum ipsius ut manifestetur illis
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
oculi mei semper ad Dominum quoniam ipse evellet de laqueo pedes meos
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
respice in me et miserere mei quia unicus et pauper sum ego
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
tribulationes cordis mei multiplicatae sunt de necessitatibus meis erue me
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
vide humilitatem meam et laborem meum et dimitte universa delicta mea
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
respice inimicos meos quoniam multiplicati sunt et odio iniquo oderunt me
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
custodi animam meam et erue me non erubescam quoniam speravi in te
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
innocentes et recti adheserunt mihi quia sustinui te
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
libera Deus Israhel ex omnibus tribulationibus suis