< Zabura 25 >

1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
[Psalm lal David] O LEUM GOD, nga sot insiuk nufon nu sum;
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
God luk, nga lulalfongi kom. Nikmet lela in akmwekinyeyuk nga. Nikmet lela mwet lokoalok luk in aksruksrukyeyu!
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Elos su tupan kom fah tia akmwekinyeyuk, A elos na su tuyak lain kom fah mwekin.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Fahkak inkanek lom nu sik, O LEUM GOD, Luti nu sik innek lom.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Lutiyu in moul fal nu ke ma pwaye lom, Tu kom God luk su moliyula. Nga lulalfongi kom pacl e nukewa.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
O LEUM GOD, esam pakoten ac lungse kawil lom Su kom akkalemye oemeet me.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Nimet esam ma sutuu ac ma koluk luk in len in fusr luk. A esamyu, O LEUM GOD, Fal nu ke lungse kawil ac pakoten lom.
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Ke sripen LEUM GOD el suwohs ac wo, El luti mwet koluk ke inkanek elos in fahsr kac.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
El kol mwet inse pusisel nu ke inkanek pwaye Ac lotelos ke ma lungse lal.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
Ke oaru ac lungse, El kololos su Karinganang wuleang lal ac akos ma sap lal.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
LEUM GOD, nunak munas ke ma koluk luk, fal nu ke Inem, Tuh ma koluk luk arulana pus.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
Elos su sunakin LEUM GOD El ac fah luti nu selos inkanek su fal elos in fahsr kac.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
Elos ac fah kapkapak, Ac fwil natulos ac fah usrui facl selos.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
LEUM GOD El mwet kawuk lalos su sunakunul Ac El ac fah akpwayeye wulela lal nu selos.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Nga suk kasru sin LEUM GOD in pacl nukewa, Ac El moliyu liki mwe sensen.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
LEUM GOD, ngetma nu sik ac pakomutuk, Tuh nga muku ac munas.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
Akfisrasrye mwe fosrnga nu sik Ac moliyula liki mwe ongoiya.
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Akilen fosrnga ac keok luk Ac nunak munas ke ma koluk luk nukewa.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Liye pusiyen mwet lokoalok luk, Ac ke lupan srunga sulallal lalos nu sik.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Karinginyu ac moliyula: Nikmet lela in akmwekinyeyuk nga, Tuh nga tuku in moulla yurum.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Lela ma wo ac suwohs luk in akwoyeyu, Mweyen nga lulalfongi in kom.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
O God, molela Israel, mwet lom, Liki mwe ongoiya lalos nukewa.

< Zabura 25 >