< Zabura 25 >

1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
ダビデの歌 主よ、わが魂はあなたを仰ぎ望みます。
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
わが神よ、わたしはあなたに信頼します。どうか、わたしをはずかしめず、わたしの敵を勝ち誇らせないでください。
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
すべてあなたを待ち望む者をはずかしめず、みだりに信義にそむく者をはずかしめてください。
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
主よ、あなたの大路をわたしに知らせ、あなたの道をわたしに教えてください。
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
あなたのまことをもって、わたしを導き、わたしを教えてください。あなたはわが救の神です。わたしはひねもすあなたを待ち望みます。
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
主よ、あなたのあわれみと、いつくしみとを思い出してください。これはいにしえから絶えることがなかったのです。
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
わたしの若き時の罪と、とがとを思い出さないでください。主よ、あなたの恵みのゆえに、あなたのいつくしみにしたがって、わたしを思い出してください。
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
主は恵みふかく、かつ正しくいらせられる。それゆえ、主は道を罪びとに教え、
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
へりくだる者を公義に導き、へりくだる者にその道を教えられる。
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
主のすべての道はその契約とあかしとを守る者にはいつくしみであり、まことである。
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
主よ、み名のために、わたしの罪をおゆるしください。わたしの罪は大きいのです。
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
主を恐れる人はだれか。主はその選ぶべき道をその人に教えられる。
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
彼はみずからさいわいに住まい、そのすえは地を継ぐであろう。
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
主の親しみは主をおそれる者のためにあり、主はその契約を彼らに知らせられる。
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
わたしの目は常に主に向かっている。主はわたしの足を網から取り出されるからである。
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
わたしをかえりみ、わたしをあわれんでください。わたしはひとりわびしく苦しんでいるのです。
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
わたしの心の悩みをゆるめ、わたしを苦しみから引き出してください。
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
わたしの苦しみ悩みをかえりみ、わたしのすべての罪をおゆるしください。
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
わたしの敵がいかに多く、かつ激しい憎しみをもってわたしを憎んでいるかをごらんください。
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
わたしの魂を守り、わたしをお助けください。わたしをはずかしめないでください。わたしはあなたに寄り頼んでいます。
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
どうか、誠実と潔白とが、わたしを守ってくれるように。わたしはあなたを待ち望んでいます。
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
神よ、イスラエルをあがない、すべての悩みから救いだしてください。

< Zabura 25 >