< Zabura 25 >
1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
Von David. Zu dir, o HERR, erhebe ich meine Seele;
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
mein Gott, ich traue auf dich; laß mich nicht zuschanden werden, daß meine Feinde nicht frohlocken über mich.
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Gar keiner wird zuschanden, der deiner harrt; zuschanden werden, die ohne Ursache treulos handeln!
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
HERR, zeige mir deine Wege und lehre mich deine Pfade;
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
leite mich durch deine Wahrheit und lehre mich; denn du bist der Gott meines Heils; auf dich harre ich allezeit.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Gedenke, o HERR, deiner Barmherzigkeit und deiner Gnade, die von Ewigkeit her sind!
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Gedenke nicht der Sünden meiner Jugend und meiner Übertretungen; gedenke aber mein nach deiner Gnade, um deiner Güte willen, o HERR.
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Der HERR ist gut und gerecht, darum weist er die Sünder auf den Weg;
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
er leitet die Elenden auf den rechten Pfad und lehrt die Elenden seinen Weg.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
Alle Pfade des HERRN sind Gnade und Wahrheit denen, die seinen Bund und seine Zeugnisse bewahren.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
Um deines Namens willen, o HERR, vergib meine Schuld; denn sie ist groß!
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
Wer ist der Mann, der den HERRN fürchtet? Er lehrt ihn den Weg, den er erwählen soll.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
Seine Seele wird im Guten wohnen, und sein Same wird das Land besitzen.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
Freundschaft hält der HERR mit denen, die ihn fürchten, und seinen Bund tut er ihnen kund.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Meine Augen sind stets auf den HERRN gerichtet, daß er meinen Fuß aus dem Netze ziehe.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Wende dich zu mir und sei mir gnädig; denn ich bin einsam und elend!
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
Erleichtere die Angst meines Herzens und führe mich heraus aus meinen Nöten!
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Siehe an mein Elend und meine Plage und vergib mir alle meine Sünden!
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Siehe an meine Feinde, denn ihrer sind viele, und sie hassen mich grimmig.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Bewahre meine Seele und rette mich; laß mich nicht zuschanden werden; denn ich traue auf dich!
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Unschuld und Redlichkeit mögen mich behüten; denn ich harre deiner.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
O Gott, erlöse Israel aus allen seinen Nöten!