< Zabura 25 >
1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
Ein Psalm Davids. Nach dir, HERR, verlangt mich.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
Mein Gott, ich hoffe auf dich; laß mich nicht zu Schanden werden, daß sich meine Feinde nicht freuen über mich.
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Denn keiner wird zu Schanden, der dein harret; aber zu Schanden müssen sie werden, die leichtfertigen Verächter.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
HERR, zeige mir deine Wege und lehre mich deine Steige;
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
leite mich in deiner Wahrheit und lehre mich! Denn du bist der Gott, der mir hilft; täglich harre ich dein.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Gedenke, HERR, an deine Barmherzigkeit und an deine Güte, die von der Welt her gewesen ist.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Gedenke nicht der Sünden meiner Jugend und meiner Übertretungen; gedenke aber mein nach deiner Barmherzigkeit um deiner Güte willen!
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Der HERR ist gut und fromm; darum unterweist er die Sünder auf dem Wege.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
Er leitet die Elenden recht und lehrt die Elenden seinen Weg.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
Die Wege des HERRN sind eitel Güte und Wahrheit denen, die seinen Bund und seine Zeugnisse halten.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
Um deines Namens willen, HERR, sei gnädig meiner Missetat, die da groß ist.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
Wer ist der, der den HERRN fürchtet? Er wird ihn unterweisen den besten Weg.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
Seine Seele wird im Guten wohnen, und sein Same wird das Land besitzen.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
Das Geheimnis des HERRN ist unter denen, die ihn fürchten; und seinen Bund läßt er sie wissen.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Meine Augen sehen stets zu dem HERRN; denn er wird meinen Fuß aus dem Netze ziehen.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Wende dich zu mir und sei mir gnädig; denn ich bin einsam und elend.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
Die Angst meines Herzens ist groß; führe mich aus meinen Nöten!
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Siehe an meinen Jammer und mein Elend und vergib mir alle meine Sünden!
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Siehe, daß meiner Feinde so viel sind und hassen mich aus Frevel.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Bewahre meine Seele und errette mich, laß mich nicht zu Schanden werden; denn ich traue auf dich.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Schlecht und Recht, das behüte mich; denn ich harre dein.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Gott, erlöse Israel aus aller seiner Not!