< Zabura 25 >
1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
Von David. - Nach Dir verlangt mich, Herr.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
Mein Gott, auf Dich nur hoffe ich. Laß nimmer mich zuschanden werden! Laß meine Feinde über mich nicht jubeln!
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Nicht einer, der auf Dich vertraut, wird je zuschanden. Doch leer gehn aus die Abgefallenen.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Belehre, Herr, mich über Deine Wege! Gewöhne mich an Deine Pfade!
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
In Deiner Treue leite mich! Gewöhne mich daran! Denn Du bist meines Heiles Gott; stets hoffe ich auf Dich. -
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Gedenke Deiner Liebe, Herr, und Güte! Sie sind von Ewigkeit.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Gedenk nicht meiner Jugendsünden, meiner Missetaten nicht! Gedenk mir dessen nur, was Deiner Gnade würdig ist, um Deiner Güte willen, Herr! -
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Der Herr ist gütig und wahrhaftig; drum zeigt er Irrenden die rechte Bahn.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
Bedrückte leitet er, wie's richtig ist, gewöhnt an seinen Weg die Dulder.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
Des Herrn Wege all' sind Lieb' und Treue für die, die seinen Bund und seine Lehren halten. -
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
Um Deines Namens willen, Herr, vergib mir meine Schuld, so groß ist sie! -
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
Ist irgendwo ein Mann in Furcht des Herrn, so zeigt er ihm den Weg, den jener wählen soll.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
Ihm ist das Glück auch hold; sein Stamm ererbt das Land.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
Des Herrn Geheimnis eignet denen, die ihn fürchten; in seinen Bund weiht er sie ein.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Mein Auge schaut stets auf den Herrn; denn meine Füße kann er vor dem Netz bewahren.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Schau her auf mich! Sei gnädig mir! Verlassen bin ich, elend.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
Erweitere mein beklemmtes Herz! Aus meinen Nöten rette mich!
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Schau meine Pein, mein Elend an! Vergib mir alle meine Sünden! -
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Betrachte meine Feinde, welche Menge, den Haß, wie furchtbar sie mich hassen!
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Mein Leben schirme, rette mich, damit ich nicht zuschanden werde! Ich harre Dein.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Mir bleibe Unschuld! Mir bleibe Redlichkeit! Ich harre Dein.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Erlöse Israel aus allen seinen Nöten, Gott!