< Zabura 25 >

1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
Psaume de David. [Aleph.] Eternel, j'élève mon âme à toi.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
[Beth.] Mon Dieu, je m'assure en toi, fais que je ne sois point confus, [et] que mes ennemis ne triomphent point de moi.
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
[Guimel.] Certes, pas un de ceux qui se confient en toi, ne sera confus; ceux qui agissent perfidement sans sujet seront confus.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
[Daleth.] Eternel! fais-moi connaître tes voies, enseigne-moi tes sentiers.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
[He. Vau.] Fais-moi marcher selon la vérité, et m'enseigne; car tu es le Dieu de ma délivrance; je m'attends à toi tout le jour.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
[Zain.] Eternel, souviens-toi de tes compassions et de tes gratuités; car elles sont de tout temps.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
[Heth.] Ne te souviens point des péchés de ma jeunesse, ni de mes transgressions; selon ta gratuité souviens-toi de moi, pour l'amour de ta bonté, ô Eternel!
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
[Teth.] L’Eternel est bon et droit, c'est pourquoi il enseignera aux pécheurs le chemin qu'ils doivent tenir.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
[Jod.] Il fera marcher dans la justice les débonnaires, et il leur enseignera sa voie.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
[Caph.] Tous les sentiers de l'Eternel [sont] gratuité et vérité à ceux qui gardent son alliance et ses témoignages.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
[Lamed.] Pour l'amour de ton Nom, ô Eternel! tu me pardonneras mon iniquité, quoiqu'elle soit grande.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
[Mem.] Qui est l'homme qui craint l'Eternel? [L'Eternel] lui enseignera le chemin qu'il doit choisir.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
[Nun.] Son âme logera au milieu des biens, et sa postérité possédera la terre en héritage.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
[Samech.] Le secret de l'Eternel est pour ceux qui le craignent, et son alliance pour la leur donner à connaître.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
[Hajin.] Mes yeux sont continuellement sur l'Eternel; car c'est lui qui tirera mes pieds du filet.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
[Pe.] Tourne ta face vers moi, et aie pitié de moi; car je suis seul, et affligé.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
[Tsade.] Les détresses de mon cœur se sont augmentées; tire-moi hors de mes angoisses.
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
[Res.] Regarde mon affliction et mon travail, et me pardonne tous mes péchés.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
[Res.] Regarde mes ennemis, car ils sont en grand nombre, et ils me haïssent d'une haine [pleine] de violence.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
[Scin.] Garde mon âme, et me délivre; [fais] que je ne sois point confus; car je me suis retiré vers toi.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
[Thau.] Que l'intégrité et la droiture me gardent; car je me suis attendu à toi.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
[Pe.] Ô Dieu! rachète Israël de toutes ses détresses.

< Zabura 25 >