< Zabura 25 >
1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
De David. À toi, Éternel, j’élève mon âme.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
Mon Dieu, en toi j’ai mis ma confiance; que je ne sois pas confus, que mes ennemis ne triomphent pas de moi.
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Non, aucun de ceux qui s’attendent à toi ne sera confus; ceux-là seront confus qui agissent perfidement sans cause.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Fais-moi connaître tes voies, ô Éternel! enseigne-moi tes sentiers.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Fais-moi marcher dans ta vérité, et enseigne-moi, car tu es le Dieu de mon salut; c’est à toi que je m’attends tout le jour.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Souviens-toi de ta miséricorde, ô Éternel, et de ta bonté; car elles sont de tout temps.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Ne te souviens pas des péchés de ma jeunesse ni de mes transgressions; selon ta gratuité souviens-toi de moi à cause de ta bonté, ô Éternel.
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
L’Éternel est bon et droit; c’est pourquoi il enseignera le chemin aux pécheurs.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
Il fera marcher dans le droit [chemin] les débonnaires, et il enseignera sa voie aux débonnaires.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
Tous les sentiers de l’Éternel sont gratuité et vérité, pour ceux qui gardent son alliance et ses témoignages.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
À cause de ton nom, ô Éternel! tu me pardonneras mon iniquité; car elle est grande.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
Qui est l’homme qui craint l’Éternel? Il lui enseignera le chemin qu’il doit choisir.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
Son âme habitera au milieu du bien, et sa semence possédera la terre.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
Le secret de l’Éternel est pour ceux qui le craignent, pour leur faire connaître son alliance.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Mes yeux sont continuellement sur l’Éternel; car c’est lui qui fera sortir mes pieds du filet.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Tourne-toi vers moi et use de grâce envers moi, car je suis seul et affligé.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
Les détresses de mon cœur se sont agrandies; fais-moi sortir de mes angoisses.
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Regarde mon affliction et mes peines, et pardonne tous mes péchés.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Regarde mes ennemis, car ils sont nombreux, et ils me haïssent d’une haine violente.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Garde mon âme, et délivre-moi; que je ne sois pas confus, car je me suis confié en toi.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Que l’intégrité et la droiture me gardent, car je me suis attendu à toi.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Ô Dieu! rachète Israël de toutes ses détresses.