< Zabura 25 >

1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
By David. Unto Thee, O Jehovah, my soul I lift up.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
My God, in Thee I have trusted, Let me not be ashamed, Let not mine enemies exult over me.
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Also let none waiting on Thee be ashamed, Let the treacherous dealers without cause be ashamed.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Thy ways, O Jehovah, cause me to know, Thy paths teach Thou me.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Cause me to tread in Thy truth, and teach me, For Thou [art] the God of my salvation, Near Thee I have waited all the day.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Remember Thy mercies, O Jehovah, And Thy kindnesses, for from the age [are] they.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Sins of my youth, and my transgressions, Do not Thou remember. According to Thy kindness be mindful of me, For Thy goodness' sake, O Jehovah.
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Good and upright [is] Jehovah, Therefore He directeth sinners in the way.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
He causeth the humble to tread in judgment, And teacheth the humble His way.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
All the paths of Jehovah [are] kindness and truth, To those keeping His covenant, And His testimonies.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
For Thy name's sake, O Jehovah, Thou hast pardoned mine iniquity, for it [is] great.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
Who [is] this — the man fearing Jehovah? He directeth him in the way He doth choose.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
His soul in good doth remain, And his seed doth possess the land.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
The secret of Jehovah [is] for those fearing Him, And His covenant — to cause them to know.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Mine eyes [are] continually unto Jehovah, For He bringeth out from a net my feet.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Turn Thou unto me, and favour me, For lonely and afflicted [am] I.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
The distresses of my heart have enlarged themselves, From my distresses bring me out.
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
See mine affliction and my misery, And bear with all my sins.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
See my enemies, for they have been many, And with violent hatred they have hated me.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Keep my soul, and deliver me, Let me not be ashamed, for I trusted in Thee.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Integrity and uprightness do keep me, For I have waited [on] Thee.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Redeem Israel, O God, from all his distresses!

< Zabura 25 >