< Zabura 25 >

1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
[A Psalm] of David. To thee, O LORD, do I lift up my soul.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
O my God, I trust in thee: let me not be ashamed, let not my enemies triumph over me,
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Also, let none that wait on thee be ashamed: let them be ashamed who transgress without cause.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Show me thy ways, O LORD; teach me thy paths.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Lead me in thy truth, and teach me: for thou [art] the God of my salvation; on thee do I wait all the day.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Remember, O LORD, thy tender mercies and thy loving kindnesses; for they [have been] ever of old.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Remember not the sins of my youth, nor my transgressions: according to thy mercy remember thou me for thy goodness' sake, O LORD.
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Good and upright [is] the LORD: therefore will he teach sinners in the way.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
The meek will he guide in judgment: and the meek will he teach his way.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
All the paths of the LORD [are] mercy and truth to such as keep his covenant and his testimonies.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
For thy name's sake, O LORD, pardon my iniquity; for it [is] great.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
What man [is] he that feareth the LORD? him shall he teach in the way [that] he shall choose.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
His soul shall dwell at ease; and his seed shall inherit the earth.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
The secret of the LORD [is] with them that fear him; and he will show them his covenant.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
My eyes [are] ever towards the LORD; for he will pluck my feet out of the net.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Turn thee to me, and have mercy upon me; for I [am] desolate and afflicted.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
The troubles of my heart are enlarged: O bring thou me out of my distresses.
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Look upon my affliction and my pain; and forgive all my sins.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Consider my enemies, for they are many; and they hate me with cruel hatred.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
O keep my soul, and deliver me: let me not be ashamed; for I put my trust in thee.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Let integrity and uprightness preserve me; for I wait on thee.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Redeem Israel, O God, out of all his troubles.

< Zabura 25 >