< Zabura 25 >

1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
Yahweh, my God, I give myself to you.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
I trust in you. Do not allow my enemies [to defeat me], with the result that I would be ashamed/disgraced. Do not allow my enemies to defeat/conquer me, with the result that they would rejoice.
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Do not allow any of those who trust in you to be disappointed/disgraced. Cause those who (act treacherously toward/try to deceive) others to be disappointed/disgraced.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Yahweh, show me the way that I should (conduct my life/live as you want me to), teach me how to act in the manner that you want me to act/behave.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Teach me to conduct my life [by obeying] your truth because you are my God, the one who saves me. All the time I trust in you.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Yahweh, do not forget how you have acted mercifully to me and have faithfully loved me; that is the way that you have acted toward me from long ago.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Forgive me for all the sinful things I did and the ways that I rebelled against you when I was young; I ask this because you faithfully love your people and do good things for them, Yahweh, do not forget me!
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Yahweh is good and fair/just; therefore he shows sinners (how they should conduct their lives/how to live as you want them to).
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
He shows humble people what is right for them to do and teaches them what he wants [them to do].
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
He always faithfully loves and does what he has promised to those who keep his agreement with them and who do what he requires.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
Yahweh, forgive me for all my sins, which are many, in order that I may honor you [MTY].
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
To all those who revere you [RHQ], you show them the (right way to conduct their lives/things that they should do).
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
They will always be prosperous, and their descendants will continue to live in [this] land.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
Yahweh is a friend of those who have an awesome respect for him, and he teaches them the agreement that he [made with them].
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
I always ask [MTY] Yahweh to help me, and he rescues me from danger [MET].
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Yahweh, pay attention to me and be merciful to me, because I am alone, and I am very distressed because I am suffering/oppressed.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
Help me to not worry, and rescue me from my troubles.
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Note that I am distressed and troubled [DOU], and forgive [me for] all my sins.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Also note that I have many enemies, see that they hate me very much.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Protect me, and rescue me from them; do not allow [them to defeat me], [with the result that] I would be ashamed/disgraced; I have come to you to (get refuge/be safe).
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Protect me because I do what is good and honest/just [PRS], and because I trust in you.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
God, rescue [us] Israeli people from all of our troubles!

< Zabura 25 >