< Zabura 25 >
1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
“A psalm of David.” To thee, O LORD! do I lift up my soul.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
O my God! I trust in thee; let me not be put to shame! Let not my enemies triumph over me!
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Yea, none that hope in thee shall be put to shame: They shall be put to shame who wickedly forsake thee.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Cause me to know thy ways, O LORD! Teach me thy paths!
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Lead me in thy truth, and teach me! For thou art the God from whom cometh my help; In thee do I trust at all times!
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Remember thy loving-kindness, O LORD! and thy tender mercy, Which thou hast exercised of old!
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Remember not the faults and transgressions of my youth! According to thy mercy remember thou me, For thy goodness' sake, O LORD!
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Good and righteous is the LORD; Therefore showeth he to sinners the way.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
The humble he guideth in his statutes, And the humble he teacheth his way.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
All the doings of the LORD are mercy and truth To those who keep his covenant and his precepts.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
For thy name's sake, O LORD, Pardon my iniquity; for it is great!
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
Who is the man that feareth the LORD? Him doth he show the way which he should choose.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
He shall himself dwell in prosperity, And his offspring shall inherit the land.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
The friendship of the LORD is with them that fear him, And he will teach them his covenant.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Mine eyes are ever directed to the LORD, For he will pluck my feet from the net.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Look upon me, and pity me; For I am desolate and afflicted!
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
Lighten the sorrows of my heart, And deliver me from my troubles!
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Look upon my affliction and distress, And forgive all my sins!
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Consider how many are my enemies, And with what violence they hate me!
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Guard thou my life, and deliver me! Let me not be put to shame, for I have trusted in thee!
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Let integrity and uprightness preserve me, For on thee do I rest my hope!
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Redeem Israel, O God! from all his troubles!