< Zabura 25 >

1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
A Psalm of David. Unto Thee, O LORD, do I lift up my soul.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
O my God, in Thee have I trusted, let me not be ashamed; let not mine enemies triumph over me.
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Yea, none that wait for Thee shall be ashamed; they shall be ashamed that deal treacherously without cause.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Show me Thy ways, O LORD; teach me Thy paths.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Guide me in Thy truth, and teach me; for Thou art the God of my salvation; for Thee do I wait all the day.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Remember, O LORD, Thy compassions and Thy mercies; for they have been from of old.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Remember not the sins of my youth, nor my transgressions; according to Thy mercy remember Thou me, for Thy goodness' sake, O LORD.
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Good and upright is the LORD; therefore doth He instruct sinners in the way.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
He guideth The humble in justice; and He teacheth the humble His way.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
All the paths of the LORD are mercy and truth unto such as keep His covenant and His testimonies.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
For Thy name's sake, O LORD, pardon mine iniquity, for it is great.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
What man is he that feareth the LORD? him will He instruct in the way that He should choose.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
His soul shall abide in prosperity; and his seed shall inherit the land.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
The counsel of the LORD is with them that fear Him; and His covenant, to make them know it.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Mine eyes are ever toward the LORD; for He will bring forth my feet out of the net.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Turn Thee unto me, and be gracious unto me; for I am solitary and afflicted.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
The troubles of my heart are enlarged; O bring Thou me out of my distresses.
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
See mine affliction and my travail; and forgive all my sins.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Consider how many are mine enemies, and the cruel hatred wherewith they hate me.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
O keep my soul, and deliver me; let me not be ashamed, for I have taken refuge in Thee.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Let integrity and uprightness preserve me, because I wait for Thee.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Redeem Israel, O God, out of all his troubles.

< Zabura 25 >