< Zabura 25 >

1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
Of David. To you, O Lord, my soul is lifted up.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
O my God, I have put my faith in you, let me not be shamed; let not my haters be glorying over me.
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
Let no servant of yours be put to shame; may those be shamed who are false without cause.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Make your steps clear to me, O Lord; give me knowledge of your ways.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Be my guide and teacher in the true way; for you are the God of my salvation; I am waiting for your word all the day.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
O Lord, keep in mind your pity and your mercies; for they have been from the earliest times.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Do not keep in mind my sins when I was young, or my wrongdoing: let your memory of me be full of mercy, O Lord, because of your righteousness.
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Good and upright is the Lord: so he will be the teacher of sinners in the way.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
He will be an upright guide to the poor in spirit: he will make his way clear to them.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
All the ways of the Lord are mercy and good faith for those who keep his agreement and his witness.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
Because of your name, O Lord, let me have forgiveness for my sin, which is very great.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
If a man has the fear of the Lord, the Lord will be his teacher in the way of his pleasure.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
His soul will be full of good things, and his seed will have the earth for its heritage.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
The secret of the Lord is with those in whose hearts is the fear of him; he will make his agreement clear to them.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
My eyes are turned to the Lord at all times; for he will take my feet out of the net.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Be turned to me, and have mercy on me; for I am troubled and have no helper.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
The troubles of my heart are increased: O take me out of my sorrows.
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Give thought to my grief and my pain; and take away all my sins.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
See how those who are against me are increased, for bitter is their hate of me.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
O keep my soul, and take me out of danger: let me not be shamed, for I have put my faith in you.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
For my clean and upright ways keep me safe, because my hope is in you.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Give Israel salvation, O God, out of all his troubles.

< Zabura 25 >