< Zabura 24 >
1 Zabura ta Dawuda. Duniya ta Ubangiji ce da kome da yake cikinta, duniya, da dukan waɗanda suke zama a cikinta;
La tierra es del Señor y su plenitud. con toda su riqueza; el mundo y todas las personas que viven en él.
2 gama ya gina ta a kan tekuna ya kafa ta a kan ruwaye.
Porque él Señor puso las bases de los mares, y la afirmó sobre los ríos profundos.
3 Wa zai iya hawan tudun Ubangiji? Wa zai iya tsaya a wurinsa mai tsarki?
¿Quién puede subir al monte del Señor? ¿y quién puede permanecer en su lugar santo?
4 Sai wanda yake da hannu mai tsabta da kuma tsabtar zuciya, wanda ba ya ba da ransa ga bautar gunki ko ya rantse bisa abin da yake ƙarya.
El que tiene las manos limpias y un corazón verdadero; él que no ha elevado su alma a cosas vanas, que no ha hecho un falso juramento.
5 Zai sami albarka daga Ubangiji da fiffitawa daga Allah Mai cetonsa.
Él tendrá la bendición del Señor, y la justicia del Dios de su salvación.
6 Irin tsaran waɗanda suke nemansa ke nan, waɗanda suke neman fuskarka, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
Esta es la generación de aquellos cuyos corazones se volvieron a ti, de los que buscan tu rostro, oh Dios de Jacob. (Selah)
7 Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
¡Ábranse puertas eternas! ¡oh puertas; quédense abiertas de par en par. puertas eternas, para que entre el Rey de la gloria!
8 Wane ne wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji ne mai ƙarfi mai iko, Ubangiji mai girma a yaƙi.
¿Quién es el Rey de la gloria? El Señor fuerte y valiente, el Señor poderoso en la guerra.
9 Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
¡Ábranse puertas eternas!, oh puertas; quédense abiertas de par en par. oh puertas eternas, para que entre el Rey de la gloria.
10 Wane ne shi, wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji Maɗaukaki, shi ne Sarkin ɗaukaka. (Sela)
¿Quién es el Rey de la gloria? El Señor de los ejércitos, él es el Rey de la gloria. (Selah)