< Zabura 24 >
1 Zabura ta Dawuda. Duniya ta Ubangiji ce da kome da yake cikinta, duniya, da dukan waɗanda suke zama a cikinta;
De Yavé es la tierra y lo que hay en ella, El mundo y los que habitan en él.
2 gama ya gina ta a kan tekuna ya kafa ta a kan ruwaye.
Porque Él la fundó sobre los mares Y la afirmó sobre las corrientes de agua.
3 Wa zai iya hawan tudun Ubangiji? Wa zai iya tsaya a wurinsa mai tsarki?
¿Quién subirá a la Montaña de Yavé? ¿Quién podrá estar en pie en su Santuario?
4 Sai wanda yake da hannu mai tsabta da kuma tsabtar zuciya, wanda ba ya ba da ransa ga bautar gunki ko ya rantse bisa abin da yake ƙarya.
El limpio de manos y puro de corazón, El que no elevó su alma a la falsedad Ni juró con engaño.
5 Zai sami albarka daga Ubangiji da fiffitawa daga Allah Mai cetonsa.
Él recibirá bendición de Yavé Y la justicia del ʼElohim de su salvación.
6 Irin tsaran waɗanda suke nemansa ke nan, waɗanda suke neman fuskarka, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
Esta es la generación de los que lo buscan, De los que buscan tu rostro, [oh] ʼElohim de Jacob. (Selah)
7 Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
¡Alcen, oh puertas, sus cabezas! ¡Sean levantados, portales eternos, Y entrará el Rey de gloria!
8 Wane ne wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji ne mai ƙarfi mai iko, Ubangiji mai girma a yaƙi.
¿Quién es este Rey de gloria? ¡Yavé, el Fuerte y Poderoso! ¡Yavé, el Poderoso en batalla!
9 Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
¡Alcen, oh puertas, sus cabezas! ¡Sean levantados, portales eternos, Y entrará el Rey de gloria!
10 Wane ne shi, wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji Maɗaukaki, shi ne Sarkin ɗaukaka. (Sela)
¿Quién es este Rey de gloria? ¡Yavé de las huestes! ¡Él es el Rey de gloria! (Selah)