< Zabura 24 >

1 Zabura ta Dawuda. Duniya ta Ubangiji ce da kome da yake cikinta, duniya, da dukan waɗanda suke zama a cikinta;
Um salmo de David. A terra é de Yahweh, com sua plenitude; o mundo, e aqueles que nele habitam.
2 gama ya gina ta a kan tekuna ya kafa ta a kan ruwaye.
Pois ele a fundou nos mares, e a estabeleceu nas enchentes.
3 Wa zai iya hawan tudun Ubangiji? Wa zai iya tsaya a wurinsa mai tsarki?
Quem pode subir a colina de Yahweh? Quem pode estar em seu lugar sagrado?
4 Sai wanda yake da hannu mai tsabta da kuma tsabtar zuciya, wanda ba ya ba da ransa ga bautar gunki ko ya rantse bisa abin da yake ƙarya.
Aquele que tem as mãos limpas e um coração puro; que não elevou sua alma à falsidade, e não jurou enganosamente.
5 Zai sami albarka daga Ubangiji da fiffitawa daga Allah Mai cetonsa.
Ele receberá uma bênção de Yahweh, justiça do Deus de sua salvação.
6 Irin tsaran waɗanda suke nemansa ke nan, waɗanda suke neman fuskarka, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
Esta é a geração daqueles que O buscam, que procuram seu rosto - mesmo o Jacob. (Selah)
7 Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
Levantem suas cabeças, seus portões! Levantem-se, suas portas eternas, e o Rei da Glória entrará.
8 Wane ne wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji ne mai ƙarfi mai iko, Ubangiji mai girma a yaƙi.
Quem é o Rei da Glória? Yahweh forte e poderoso, Yahweh poderoso em batalha.
9 Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
Levantem a cabeça, seus portões; Sim, levantem-nas, suas portas eternas, e o Rei da Glória entrará.
10 Wane ne shi, wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji Maɗaukaki, shi ne Sarkin ɗaukaka. (Sela)
Quem é este rei da glória? Javé dos Exércitos é o Rei da Glória! (Selah)

< Zabura 24 >