< Zabura 24 >

1 Zabura ta Dawuda. Duniya ta Ubangiji ce da kome da yake cikinta, duniya, da dukan waɗanda suke zama a cikinta;
Av David; en salme. Jorden hører Herren til - og alt det som fyller den, jorderike og de som bor der.
2 gama ya gina ta a kan tekuna ya kafa ta a kan ruwaye.
For han har grunnlagt den på hav og stilt den fast på strømmer.
3 Wa zai iya hawan tudun Ubangiji? Wa zai iya tsaya a wurinsa mai tsarki?
Hvem skal stige op på Herrens berg, og hvem skal stå på hans hellige sted?
4 Sai wanda yake da hannu mai tsabta da kuma tsabtar zuciya, wanda ba ya ba da ransa ga bautar gunki ko ya rantse bisa abin da yake ƙarya.
Den som har uskyldige hender og et rent hjerte, som ikke har vendt sin hu til løgn og ikke har svoret falskelig.
5 Zai sami albarka daga Ubangiji da fiffitawa daga Allah Mai cetonsa.
Han skal motta velsignelse fra Herren og rettferdighet fra sin frelses Gud.
6 Irin tsaran waɗanda suke nemansa ke nan, waɗanda suke neman fuskarka, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
Dette er deres ætt som spør efter ham, de som søker ditt åsyn, Jakobs barn. (Sela)
7 Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
Løft, I porter, eders hoder, og løft eder, I evige dører, så herlighetens konge kan dra inn!
8 Wane ne wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji ne mai ƙarfi mai iko, Ubangiji mai girma a yaƙi.
Hvem er den herlighetens konge? Herren, sterk og veldig, Herren veldig i strid.
9 Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
Løft, I porter, eders hoder, og løft eder, I evige dører, så herlighetens konge kan dra inn!
10 Wane ne shi, wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji Maɗaukaki, shi ne Sarkin ɗaukaka. (Sela)
Hvem er den herlighetens konge? Herren, hærskarenes Gud, han er herlighetens konge. (Sela)

< Zabura 24 >