< Zabura 24 >

1 Zabura ta Dawuda. Duniya ta Ubangiji ce da kome da yake cikinta, duniya, da dukan waɗanda suke zama a cikinta;
Of David. A psalm. The earth is the Lord’s and all that it holds, the world and those who live in it.
2 gama ya gina ta a kan tekuna ya kafa ta a kan ruwaye.
For he founded it on the seas, and on the floods he sustains it.
3 Wa zai iya hawan tudun Ubangiji? Wa zai iya tsaya a wurinsa mai tsarki?
Who may ascend the hill of the Lord? Who may stand in his holy place?
4 Sai wanda yake da hannu mai tsabta da kuma tsabtar zuciya, wanda ba ya ba da ransa ga bautar gunki ko ya rantse bisa abin da yake ƙarya.
The clean of hands, the pure of heart, who sets not their heart upon sinful things, nor swears with intent to deceive:
5 Zai sami albarka daga Ubangiji da fiffitawa daga Allah Mai cetonsa.
they win from the Lord a blessing: God is their champion and savior.
6 Irin tsaran waɗanda suke nemansa ke nan, waɗanda suke neman fuskarka, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
Such must be those who resort to him, and seek the face of the God of Jacob. (Selah)
7 Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
Lift high your heads, you gates – Higher, you ancient doors; welcome the glorious king.
8 Wane ne wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji ne mai ƙarfi mai iko, Ubangiji mai girma a yaƙi.
“Who is the glorious king?” “The Lord strong and heroic, the Lord heroic in battle.”
9 Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
Lift high your heads, you gates – Higher, you ancient doors; welcome the glorious king.
10 Wane ne shi, wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji Maɗaukaki, shi ne Sarkin ɗaukaka. (Sela)
“Who is the glorious king?” “The Lord, the God of hosts, he is the glorious king.” (Selah)

< Zabura 24 >