< Zabura 24 >

1 Zabura ta Dawuda. Duniya ta Ubangiji ce da kome da yake cikinta, duniya, da dukan waɗanda suke zama a cikinta;
“A psalm of David.” The earth is the LORD'S, and all that is therein; The world, and they who inhabit it.
2 gama ya gina ta a kan tekuna ya kafa ta a kan ruwaye.
For he hath founded it upon the seas, And established it upon the floods.
3 Wa zai iya hawan tudun Ubangiji? Wa zai iya tsaya a wurinsa mai tsarki?
Who shall ascend the hill of the LORD? And who shall stand in his holy place?
4 Sai wanda yake da hannu mai tsabta da kuma tsabtar zuciya, wanda ba ya ba da ransa ga bautar gunki ko ya rantse bisa abin da yake ƙarya.
He that hath clean hands and a pure heart; Who hath not inclined his soul to falsehood, Nor sworn deceitfully.
5 Zai sami albarka daga Ubangiji da fiffitawa daga Allah Mai cetonsa.
He shall receive a blessing from the LORD, And favor from the God of his salvation.
6 Irin tsaran waɗanda suke nemansa ke nan, waɗanda suke neman fuskarka, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
This is the race of them that seek him; They that seek thy face are Jacob. (Pause)
7 Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
Lift up your heads, O ye gates! Lift yourselves up, ye everlasting doors, That the king of glory may come in!
8 Wane ne wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji ne mai ƙarfi mai iko, Ubangiji mai girma a yaƙi.
“Who is this king of glory?” Jehovah, strong and mighty; Jehovah, mighty in battle.
9 Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
Lift up your heads, O ye gates! Lift yourselves up, ye everlasting doors, That the king of glory may enter in!
10 Wane ne shi, wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji Maɗaukaki, shi ne Sarkin ɗaukaka. (Sela)
“Who is this king of glory?” Jehovah, God of hosts, he is the king of glory. (Pause)

< Zabura 24 >