< Zabura 24 >
1 Zabura ta Dawuda. Duniya ta Ubangiji ce da kome da yake cikinta, duniya, da dukan waɗanda suke zama a cikinta;
A Psalm of David. The earth is the LORD'S, and the fulness thereof; the world, and they that dwell therein.
2 gama ya gina ta a kan tekuna ya kafa ta a kan ruwaye.
For He hath founded it upon the seas, and established it upon the floods.
3 Wa zai iya hawan tudun Ubangiji? Wa zai iya tsaya a wurinsa mai tsarki?
Who shall ascend into the mountain of the LORD? and who shall stand in His holy place?
4 Sai wanda yake da hannu mai tsabta da kuma tsabtar zuciya, wanda ba ya ba da ransa ga bautar gunki ko ya rantse bisa abin da yake ƙarya.
He that hath clean hands, and a pure heart; who hath not taken My name in vain, and hath not sworn deceitfully.
5 Zai sami albarka daga Ubangiji da fiffitawa daga Allah Mai cetonsa.
He shall receive a blessing from the LORD, and righteousness from the God of his salvation.
6 Irin tsaran waɗanda suke nemansa ke nan, waɗanda suke neman fuskarka, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
Such is the generation of them that seek after Him, that seek Thy face, even Jacob. (Selah)
7 Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
Lift up your heads, O ye gates, and be ye lifted up, ye everlasting doors; that the King of glory may come in.
8 Wane ne wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji ne mai ƙarfi mai iko, Ubangiji mai girma a yaƙi.
'Who is the King of glory?' 'The LORD strong and mighty, the LORD mighty in battle.'
9 Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
Lift up your heads, O ye gates, yea, lift them up, ye everlasting doors; that the King of glory may come in.
10 Wane ne shi, wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji Maɗaukaki, shi ne Sarkin ɗaukaka. (Sela)
'Who then is the King of glory?' 'The LORD of hosts; He is the King of glory.' (Selah)