< Zabura 24 >
1 Zabura ta Dawuda. Duniya ta Ubangiji ce da kome da yake cikinta, duniya, da dukan waɗanda suke zama a cikinta;
En Psalme af David. Herrens er Jorden og dens Fylde, Jorderige og de, der bo derpaa.
2 gama ya gina ta a kan tekuna ya kafa ta a kan ruwaye.
Thi han grundfæstede den paa Havene og gjorde den fast over Strømmene.
3 Wa zai iya hawan tudun Ubangiji? Wa zai iya tsaya a wurinsa mai tsarki?
Hvo skal gaa op paa Herrens Bjerg? hvo skal staa paa hans hellige Sted?
4 Sai wanda yake da hannu mai tsabta da kuma tsabtar zuciya, wanda ba ya ba da ransa ga bautar gunki ko ya rantse bisa abin da yake ƙarya.
Den, som har uskyldige Hænder og er ren af Hjertet; den, som ikke har sat sin Hu til Løgn og ej svoret svigeligt.
5 Zai sami albarka daga Ubangiji da fiffitawa daga Allah Mai cetonsa.
Han skal annamme Velsignelse fra Herren og Retfærdighed fra sin Frelses Gud.
6 Irin tsaran waɗanda suke nemansa ke nan, waɗanda suke neman fuskarka, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
Dette er den Slægt, som spørger efter ham, de, som søge dit Ansigt, Jakobs Børn. (Sela)
7 Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
I Porte, opløfter eders Hoveder, ja, opløfter eden, I evige Døre, at Ærens Konge kan drage ind!
8 Wane ne wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji ne mai ƙarfi mai iko, Ubangiji mai girma a yaƙi.
Hvo er denne Ærens Konge? Herren, stærk og mægtig, Herren, mægtig i Strid.
9 Ku ɗaga kawunanku, ya ku ƙofofi; ku ɗagu, ku daɗaɗɗun ƙofofi, don Sarkin ɗaukaka yă shiga.
I Porte, opløfter eders Hoveder, ja opløfter eder, I evige Døre, at Ærens Konge kan drage ind!
10 Wane ne shi, wannan Sarkin ɗaukaka? Ubangiji Maɗaukaki, shi ne Sarkin ɗaukaka. (Sela)
Hvo er han, den Ærens Konge? Herren Zebaoth, han er Ærens Konge. (Sela)