< Zabura 23 >

1 Zabura ta Dawuda. Ubangiji ne yake kiwona, ba zan rasa kome ba,
Psaume de David. L’Éternel est mon berger: je ne manquerai de rien.
2 Yakan sa in kwanta a makiyaya mai ɗanyar ciyawa, yakan bi da ni kusa da ruwaye marar hayaniya,
Il me fait reposer dans de verts pâturages, il me mène à des eaux paisibles.
3 yakan maido da raina. Yakan bi da ni a hanyoyin adalci saboda sunansa.
Il restaure mon âme; il me conduit dans des sentiers de justice, à cause de son nom.
4 Ko da na yi tafiya ta kwari na inuwar mutuwa, ba zan ji tsoron mugu ba, gama kana tare da ni; bulalarka na dūka da kuma sandanka na tafiya, za su yi mini ta’aziyya.
Même quand je marcherais par la vallée de l’ombre de la mort, je ne craindrai aucun mal; car tu es avec moi: ta houlette et ton bâton, ce sont eux qui me consolent.
5 Ka shirya mini tebur a gaban abokan gābana. Ka shafe kaina da mai; kwaf nawa ya cika har yana zuba.
Tu dresses devant moi une table, en la présence de mes ennemis; tu as oint ma tête d’huile, ma coupe est comble.
6 Tabbatacce alheri da ƙauna za su bi dukan kwanakin raina, zan kuwa zauna a gidan Ubangiji har abada.
Oui, la bonté et la gratuité me suivront tous les jours de ma vie, et mon habitation sera dans la maison de l’Éternel pour de longs jours.

< Zabura 23 >