< Zabura 23 >

1 Zabura ta Dawuda. Ubangiji ne yake kiwona, ba zan rasa kome ba,
“A psalm of David.” The LORD is my shepherd: I shall not want.
2 Yakan sa in kwanta a makiyaya mai ɗanyar ciyawa, yakan bi da ni kusa da ruwaye marar hayaniya,
He maketh me to lie down in green pastures; He leadeth me beside the still waters.
3 yakan maido da raina. Yakan bi da ni a hanyoyin adalci saboda sunansa.
He reviveth my soul; He leadeth me in paths of safety, For his name's sake.
4 Ko da na yi tafiya ta kwari na inuwar mutuwa, ba zan ji tsoron mugu ba, gama kana tare da ni; bulalarka na dūka da kuma sandanka na tafiya, za su yi mini ta’aziyya.
When I walk through a valley of deathlike shade, I fear no evil; for thou art with me; Thy crook and thy staff, they comfort me.
5 Ka shirya mini tebur a gaban abokan gābana. Ka shafe kaina da mai; kwaf nawa ya cika har yana zuba.
Thou preparest a table before me In the presence of mine enemies. Thou anointest my head with oil; My cup runneth over.
6 Tabbatacce alheri da ƙauna za su bi dukan kwanakin raina, zan kuwa zauna a gidan Ubangiji har abada.
Surely goodness and mercy shall follow me all the days of my life, And I shall dwell in the house of the LORD for ever.

< Zabura 23 >