< Zabura 23 >
1 Zabura ta Dawuda. Ubangiji ne yake kiwona, ba zan rasa kome ba,
(En salme af David.) HERREN er min Hyrde, mig skal intet fattes,
2 Yakan sa in kwanta a makiyaya mai ɗanyar ciyawa, yakan bi da ni kusa da ruwaye marar hayaniya,
han lader mig ligge på grønne Vange. Til Hvilens Vande leder han mig, han kvæger min Sjæl,
3 yakan maido da raina. Yakan bi da ni a hanyoyin adalci saboda sunansa.
han fører mig ad rette Veje for sit Navns Skyld.
4 Ko da na yi tafiya ta kwari na inuwar mutuwa, ba zan ji tsoron mugu ba, gama kana tare da ni; bulalarka na dūka da kuma sandanka na tafiya, za su yi mini ta’aziyya.
Skal jeg end vandre i Dødsskyggens Dal, jeg frygter ej ondt; thi du er med mig, din Kæp og din Stav er min Trøst.
5 Ka shirya mini tebur a gaban abokan gābana. Ka shafe kaina da mai; kwaf nawa ya cika har yana zuba.
I mine Fjenders Påsyn dækker du Bord for mig, du salver mit Hoved med Olie, mit Bæger flyder over.
6 Tabbatacce alheri da ƙauna za su bi dukan kwanakin raina, zan kuwa zauna a gidan Ubangiji har abada.
Kun Godhed og Miskundhed følger mig alle mine Dage, og i HERRENs Hus skal jeg bo gennem lange Tider.